Logo Lanfrica

Bitar Tasirin Musulunci a Kan Al’adun Hausawa na Mutuwa

Domain:

natural language processing
Creator:
AbuMusa, ShehuRab
Publisher:
SAS
Host:
Manufar wannan bincike ita ce nazarin ƙwaƙƙwafi domin gano nau’ukan tasirin da addinin Musulunci ya yi wa al’adun Hausawa na mutuwa. An yi amfani da dabarun sanya ido da nazartar kundatattun rubuce-rubuce domin tattara bayanai. An ɗora aikin kan fahimtar Hausawa ta “idan mai wuri ya zo, mai tabarma sai ya naɗe.” Sakamakon binciken ya gano cewa, tasirin Musuluncin bai kawar da dukkannin al’adun Hausawa na mutuwa ba. A maimakon haka, lamarin ya kasu gida huɗu, inda aka samu al’adun mutuwa (i) amintattu da (ii) gyararru da (iii) korarru da (iv) sauyayyu da (v) 'yan kunnen ƙashi. Daga ƙarshe binciken ya nuna dacewar nazartar dalilan da suke sa ake ci gaba da riƙo da waɗansu daga cikin al’adun mutuwa har ya zuwa yau, ƙarni na ashirin da ɗaya (Ƙ21).